Isa ga babban shafi
Amurka

China ta fusata game da tattaunawar Trump da shugabar yankin Taiwan

China ta ce matakin da zababben shugaban Amurka Donald Trump ya dauka na yin tattaunawa kai-tsaye ta wayar tarho da shugabar yankin Taiwan, abu ne da ba zai iya canza matsayin wannan yanki ba, wanda China ke kallo a matsayin wani bangare na kasarta.

Zababben shugaban Amurka Donald Trump
Zababben shugaban Amurka Donald Trump REUTERS/Carlo Allegri/File Photo
Talla

Wannan dai ya kasance karo na farko a cikin shekaru 37 da wani shugaba na Amurka ya tattaunawa ta wayar tarho kai tsaye da shugaban yankin na Taiwan, bayan da aka yanke alakar diflomasiyya ta kai-tsaye tsakanin Amurka da Taiwan.

Trump dai ya bayyana a shafinsa na Tweeter cewa, shugabar yankin na Taiwan Tsai Ing-wen ta kira shi ta waya domin taya shi murnar nasara a zaben da ya lashe.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.