Isa ga babban shafi
Korea ta Arewa

Korea ta Arewa ta sake gwajin makami mai linzami

Korea ta Arewa ta sake gwajin makami mai linzami da safiyar yau Lahadi wanda ke kasancewa karon farko tun bayan da shugaba Amurka Donald Trump ya dare karagar mulki.

Korea ta Arewa ta ki dai na gudanar da gwajin Makami mai linzami duk da gargadi MDD
Korea ta Arewa ta ki dai na gudanar da gwajin Makami mai linzami duk da gargadi MDD wikimedia.org
Talla

Hukumomin Korea ta Kudu mai makwabtaka da ita ne suka tabbatar da hakan, inda suka ce makamin da aka harba ya yi nisan zangon kilomita dari biyar kuma ya nufi Tekun Japan.

A wata ganawa da shugaban Amurka Donald Trump, Firaministan Japan Shinzo Abe, ya ce ba za a amince da wannan hallayar ta Korea ta Arewa ba, inda shugaba Trump ya ba shi tabbacin goyon baya.

Korea ta Arewa dai ta gwada makamai masu linzami da kuma nukiliya da dama a shekarar da ta gabata duk da gargadi Majalisar Dinkin Duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.