Isa ga babban shafi
Isra'ila-MDD

Isra'ila ta ki mutunta kudirin MDD a Falasdinu

Isra’ila ta yi watsi da kudirin Majalisar Dinkin Duniya da ya haramta ma ta ci gaba da gine-gine a yankin al’ummar Falasdinawa, kamar yadda Jakadan Majalisar a yankin gabas ta Tsakiya Nickolay Mladenov ya sanar. 

Wasu daga cikin gine-ginen Isra'ila a yankin Yamman ga kogin Jordan
Wasu daga cikin gine-ginen Isra'ila a yankin Yamman ga kogin Jordan Reuters/Ammar Awad
Talla

Mladenov ya ce, duk da dai Kwamitin Sulhun ya gabatar da kudirin dakatar da gine-ginen a ranar 23 ga watan Disamban bara, babu wasu matakai da aka dauka.

A cikin watan Janairun daya gabata ne gwamnatin Isra’ila ta sanar da fadada gine-ginenta fiye da dubu 6 a yankin Yamma ga Kogin Jordan da kuma gabashin birnin Kudus da ta mamaye.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.