Isa ga babban shafi
Ecuador

Dan takaran zabe a Ecuador ya yi zargin tafka magudi

Dan takaran zaben shugaban kasar Ecuador Guillermo Lasso ya yi zargin tafka magudi a zaben shugaban kasar zagaye na biyu da aka yi, inda ya sha alwashin kalubalantar sakamakon da ya baiwa Lenin Moreno nasara.

Lenín Moreno, Dan takara da ya lashe zaben kasar Ecuador
Lenín Moreno, Dan takara da ya lashe zaben kasar Ecuador Foto: AFP
Talla

Hukumar zaben kasar ta bayyana Moreno, dan takarar shugaban kasar mai barin gado, Rafael Correa, a matsayin wanda ya samu sama da kashi 51, yayin da Lasso ya samu sama da kashi 48.

Lasso ya bayyana cewar za su kare kuri’ar jama’ar kasar dan tabbatar da cewar ba a tauye musu hakki ba.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.