Ecuador
Dan takaran zabe a Ecuador ya yi zargin tafka magudi
Dan takaran zaben shugaban kasar Ecuador Guillermo Lasso ya yi zargin tafka magudi a zaben shugaban kasar zagaye na biyu da aka yi, inda ya sha alwashin kalubalantar sakamakon da ya baiwa Lenin Moreno nasara.
Wallafawa ranar:
Talla
Hukumar zaben kasar ta bayyana Moreno, dan takarar shugaban kasar mai barin gado, Rafael Correa, a matsayin wanda ya samu sama da kashi 51, yayin da Lasso ya samu sama da kashi 48.
Lasso ya bayyana cewar za su kare kuri’ar jama’ar kasar dan tabbatar da cewar ba a tauye musu hakki ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu