Colombia
Mutane 254 ne suka mutu a Mocoa na kasar Colombia
Shugaban kasar Colombia Juan Manuel Santos ya bayyana cewar ya zuwa yanzu mutane 254 aka tabbatar da mutuwar su a garin Mocoa sakamakon tsananin ruwan sama da ya haifar da zabtarewar laka.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Shugaban da ya ziyarci garin dan sa ido a aikin agaji, ya ce adadin na iya tashi ganin irin ta’adin da aka samu, yayin da ake ci gaba da neman mutanen da kasar ta birne.
Ya zuwa yanzu iyalai da dama sun bayyana cewar ba su ji duriyar yan uwan su da hadarin ya ritsa da su ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu