Shugaban Amurka ya Gayyaci Takwaransa na Philippines
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya mika goron gayyata ga takwaransa na kasar Phillippines don ya je Amurka su yi magana gaba da gaba, bayan sun tattauna ta wayan talho gameda barazanar kasar Korea ta Arewa dake ayyukan Nukiliya.
Wallafawa ranar:
Shugabannin kasashen biyu sun tattauna yakin da shugaban Philippines ke yi da masu fataucin miyagun kwayoyi, inda ba sani ba sabo kashe masu wannan sana’a kawai shugaban ke yi.
Majiyoyi na cewa shugaban Amurka Donald Trump ya ji dadin tattaunawan da yayi da shugaban Philippines Rodrigo Duterte har ya nemi takwaran na sa da ya kai ziyara Amurka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu