Philippines-Amurka
Ba lallai na amsa gayyatar Trump ba- Duterte
Shugaban Kasar Philippines Rodrigo Duterte ya ce mai yiwuwa ya ki amsa gayyatar Donald Trump na zuwa Amurka dan ganawa da shi.
Wallafawa ranar:
Talla
Duterte wanda ya karfafa dangantakarsa da tsakanin Philippines da China da Rasha, ya ce ba zai mika kai bori ya hau ba ga kasar ta Amurka.
Sai dai shugaban ya ce huldar diflomasiya tsakanin kasar sa da Amurka ta inganta bayan tafiyar shugaba Barack Obama.
Tsohon shugaban na Amurka ya yi mummunar suka kan yadda Duterte ke kashe mutane baji ba gani da sunan yaki da masu safarar miyagun kwayoyi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu