Isa ga babban shafi
Duniya

Kasashen da aikin Jarida ya fi hatsari a Duniya

Yau ce Majalisar Dinkin Duniya ta ware a matsayin ranar kare hakkin ‘Yan Jaridu ta Duniya, inda masana da ma’aikata ke nazari irin ci gaban da aka samu da kuma akasin haka.

Jaridun Faransa
Jaridun Faransa REUTERS/Regis Duvignau
Talla

Kungiyar da ke kare hakkokin 'Yan Jaridu ta bayyana kasar Mexico a matsayin mafi hadari ga ‘Yan Jaridu, ganin yadda aka kashe sama da 50 a cikin shekaru 7.

Bincike ya nuna cewar Gwamnatoci da kungiyoyin 'Yan Siyasa da kuma 'Yan ta’adda ke kai hari ko dirar mikiya kan 'Yan Jaridun dan hana fadawa mutane gaskiya.

Kungiyar ta bayyana wasu kasashen Afirka da aikin Jarida ke fuskantar hadari da suka hada da Masar da Tunisia da Tanzania da Kamaru da Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo da kuma Burundi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.