Isa ga babban shafi
Lafiya

An zabi sabon shugaban hukumar kula da lafiya WHO

An zabi Tedros Adhanom na kasar Habasha a matsayin sabon shugaban hukumar lafiya ta duniya, WHO. 

Tedros Adhanom sabon shugaban hukumar kula da lafiya da Duniya WHO.
Tedros Adhanom sabon shugaban hukumar kula da lafiya da Duniya WHO. AFP PHOTO/JOSHUA LOTT
Talla

Tedros wanda tsohon ministan lafiya ne a Habasha ya doke David Nabarro na Britaniya da Sania Nishtar ta Pakistan da sukayi takarar tare.

A wata sanarwa da ta fitar, Hukumar lafiya ta WHO ta tabbatar da Tedros a matsayin wanda ya yi nasara bayan zagaye na 3 na zaben da aka gudanar.

Tedros mai shekaru 52, kwarare a fanin kula da ciwon zazaben cizon sauro, ya kuma maye gurbin Magret Chan ta Hong Kong, wadda shugabancinta ya gamu da suka kan yadda a baya ta tunkari cutar Ebola a yammcin Afrika.

A jawabinsa na karshe kafin kada kuri’a Tedros ya lashi takobin bijiro da sabbin tsare-tsare da zai inganta sha’ani kiwon lafiya, wanda ake ganin hukumar ta gaza a kansu.

Akwai kuma batun tsarin kiwon lafiya na bai-daya da ya yi alkawarin samarwa, musamman a yankunan da talauci ya fi tsanani, musamman a kasashe masu tasowa.

Tedros ya kara da cewa, ba zai amince mutane su ke mutuwa saboda dalilai na talauci ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.