Isa ga babban shafi
Syria

Rasha ta ce mai yiyuwa ne ta kashe al-Baghdadi

Rasha ta ce tana tunanin dakarunta sun kashe jagoran kungiyar IS Abu Bakr al Baghdadi da ke da’awar jihadi a Syria da Iraqi a wani hari da suka kai a Raqqa.

Abou Bakr al-Baghdadi, a watan yulin 2014.
Abou Bakr al-Baghdadi, a watan yulin 2014. REUTERS/Social Media Website via Reuters TV
Talla

Rundunar sojin Rasha ta ce tana bincike domin tabbatar da yiyuwar mutuwar jagoran kungiyar ‘yan ta’addan da ake kira Daesh.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Rundunar sojin Rasha ta ce akwai yiyuwar al-Baghdadi na daga cikin mutanen da aka kashe a wani hari da aka kai kusa da Raqqa na Syria a ranar 28 ga watan mayun da ya gabata.

Sanarwa tace an kai harin ne a lokacin da shugaban na IS ya tara mayakansa yana tsara dubarun ficewa daga yankin na Raqqa da ake wa luguden wuta ta sama.

Sanarwar ta kara da cewa manyan kwamandojin IS kusan 30 da mayakan kungiyar 300 aka kashe.

Sai dai rundunar ta Rasha ta ce tana ci gaba da tattara bayanai domin tabbatar da hakikanin gaskiyar abin da ya faru.

Amurka ta ce ba za ta yi gaggawar tabbatar da rahoton mutuwar Baghdadi ba.

Idan har labarin ya tabbata, hakan zai kasance babbar nasara ga Rasha wadda ta kaddamar da yaki da ayyukan ta’addancin IS musamman a Syria.

A cikin dare ne aka kai harin ta sama, kuma cikin wadanda aka kashe har da Sarkin Ragga da babban jami’in tsaron IS, a cewar Rasha.

An dade dai ana ikirarin kisan Baghdadi, ko raunata shi, wanda hakan ya sa ake wa jagoran na IS kirari da sunan fatalwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.