Isa ga babban shafi
Amurka-Korea ta Arewa

Amurka da China sun tattauna barazanar Koriya ta Arewa

An yi wata tattaunawa tsakanin manyan jami’an gwamnatin Amurka da na China kan barazanar Koriya ta arewa na mallakar makaman nukiliya. Tattaunawar na zuwa bayan shugaba Donald Trump ya bayyana cewa China ta gaza shawo kan gwamnatin Pyongyang game da dakatar da shirinta na mallakar makaman.

Jami'an gwamnatin Amurka na tattaunawa da takwarorinsu na China game da Koriya ta arewa
Jami'an gwamnatin Amurka na tattaunawa da takwarorinsu na China game da Koriya ta arewa REUTERS/Aaron P. Bernstein
Talla

Sakataren harakokin wajen Amurka Rex Tillerson da na tsaro Jim Mattis ne suka yi tattaunawar da takwarorinsu na China.

Amurka ta ce babbar manufar ganawar ita ce tabbatar wa China bukatar janyo hankalin gwamnatin Kim Jong-Un na ya jingine shirin kasarsa na mallakar makaman nukiliya.

Tun rantsar da Donald Trump ya bayyana cewa dakatar da barazanar nukiliyar Koriya ne babban abin da zai sa gaba a manufofinsa na kasashen ketare, ta hanyar neman taimakon china.

Sai dai kafin soma tattaunawar da aka gudanar a jiya Laraba tsakanin Amurka da China shugaba Trump ya fito a Twitter yana cewa China ta gaza duk da ya yaba da kokarin shugaba Xi Jinping akan Koriya, amma a cewarsa haka ba ta cimma ruwa ba.

Trump dai bai fadi abin da zai iya biyo wa baya ba idan har China ta gaza shawo kan aminiyarta Koriya ta arewa kan bukatar Amurka na dakatar da shirin nukiliya da mallakar makamai masu linzame.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.