An samu zabtarewar kasa a China
Kimanin mutane 141 suka bata sakamakon zabtarewar kasa da aka samu a kasar China da ya yi sanadiyar birne gidaje sama da 40 tare a wani gari dake lardin Sichuan a kudu maso yammacin kasar.
Wallafawa ranar:
Al’amarin ya shafi yankin Sichaun, inda rahotanni suka ce zabtarewar ta janyo rusa gidaje da dama.
Masu aikin agaji da dama ne aka tura domin ceto wadanda hadarin ya ritsa da su. Amma ruwan sama na kawo tsaiku ga aikin kamar yadda Kamfanin dillacin labaran China Xinhua ya ruwaito.
Ma’aikatar kula da filaye ta danganta matsalar da rashin ajiye kasar da ake gini ta hanyar da ya dace.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu