Turkiya- Saudiya- Qatar
Shugaban Turkiya Ya Tafi Saudiya Saboda Sasanta Rikicin Kasashen Larabawa
Shugaban kasar Turkiya Recep Tayip Erdogan na shirin fara wata ziyara ta kwanaki biyu a kasar Saudiya yau Lahadi domin tattauna yadda za’a kawo karshen rikici tsakanin manyan kasashen Larabawa hudu da kuma kasar Qatar.
Wallafawa ranar:
Talla
A yau ake sa ran Shugaban Turkiya ya sauka a Saudiya inda zai gana da Sarki Salman na Saudiya, kafin ya tafi kasar Kuwait wadda take shiga tsakani daga nan kuma ya tafi kasar Qatar.
Ya fadi bayan sallar Juma’a shekaranjiya cewa zai ga lallai an warware takaddamar da ta kunno kai tsakanin kasashen na Larabawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu