Iran ta yi barazanar ficewa daga Yarjejeniyar Nukiliya
Iran ta ce tana iya ficewa daga yarjejeniyar nukiliyar da ta kulla da wasu kasashen Yammacin duniya muddin kasar Amurka ta ci gaba da sanya mata takunkumi.
Wallafawa ranar:
Shugaban kasar Hassan Rouhani ya ce matsin lamba da takunkumi ya sanya gwamnatocin da suka gabata hawan teburin tattaunawa domin samun maslaha.
Rouhani ya ce muddin Amurka zata koma irin wadannan halaye, toh Iran cikin kan-kanin lokaci zata fice daga yarjejeniyar da ta kulla domin komawa gidan jiya.
A shekarar 2015 Iran ta cim-ma Yarjejeniyar Nukuliya da kasashen duniya tare da dage mata wasu takukuman tattalin arziki da aka kakkaba ma ta a tsawon shekaru.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu