Isa ga babban shafi
Philippines

Kawo karshen masu safarar hodar ibilis a Philippines

Yan sandan kasar Philippines sun halaka wasu mutane 13 bisa samunsu da laifin tu’ammuli da miyagun kwayoyi, lamarin da ya kara yawan wadanda ‘yan sandan suka halaka zuwa 80 a cikin mako guda.

Shugaban kasar Philippines Rodrigo Duterte tareda wasu mayan hafsan sojan kasar
Shugaban kasar Philippines Rodrigo Duterte tareda wasu mayan hafsan sojan kasar Reuters
Talla

Shugaban kasar Rodrigo Duterte ya bada umarnin matsa kaimi wajen kawo karshen miyagun kwayoyi a kasar.

A farkon makon da muke ciki, akalla masu tu’ammulin da miyagun kwayoyi 67 ‘yan sandan kasar ta Philippines suka bindige, yayinda da suka kame wasu 200 a babban birnin kasar Manilam da sauran lardunan kasar.

Matakin da mataimakiyar shugaban kasar ta Philippines Leni Robredo ta yi Ala wadai da shi, a matsayin take hakkin bil adam.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.