'Yan Sandan Jamus Sun Fasa Garken Masu kulla Auren Jabu Tsakanin Maza 'Yan Najeriya Da Mata Yan Portugal
‘Yan Sanda a Jamus sun fasa garken wasu ‘yan danfara dake kulla auren karya tsakanin mata ‘yan kasar Potugal da maza ‘yan Najeriya domin samun takardun izinin zama a kasashen Turai.
Wallafawa ranar:
‘Yan Sandan Jamus sun bayyana cewa suna tsare da mutane biyar da suka hada da mata hudu a lokacin da aka kai samame a wurare 40 dake sassan kasar Jamus.
Majiyoyi sun bayyana cewa dubban kudade ake kashewa wajen auren zamba.
Masu bincike sun bayyana cewa masu kulla irin wannan aure kan dibo mata daga kasar Portugal, yayin da ake karban dubban kudade daga 'yan Najeriya domin kulla aure da ‘yar Portugal.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu