Isa ga babban shafi

"An samu raguwar rasa rayukan 'Yan Jaridu a 2017"

Rahoton da kungiyar kare hakkin ‘Yan Jaridu ta Reporters Sans Frontieres ta fitar a wannan Talata, ya ce an kashe ‘Yan Jaridu da sauran ma’aikatan yada labarai 65 a sassan duniya cikin shekara ta 2017 da ke gaf da kawo karshe.

Daya daga cikin 'Yan Jaridu da ke dauko rahoto a kasar Iraqi
Daya daga cikin 'Yan Jaridu da ke dauko rahoto a kasar Iraqi REUTERS/Mahmoud Raouf Mahmoud
Talla

Kungiyar ta ce rahoton, na nuni da cewa shekarar bana an samu karancin rasa rayukan ‘yan jarida, idan aka kwatanta da sauran shekaru 14 da aka shafe na baya-bayan nan.

Rahoton ya danganta samun rangwamen hasarar rayukan ‘Yan Jaridun, da yadda ma’aikatan yada labarai suka janye daga mafi yawan kasashen da ke fama da tashe-tashen hankula.

Har yanzu dai Syria ce kasa mafi hadari ga ma’aikatan kafafen yada labarai, inda a wannan shekara ‘Yan Jarida 12 suka hallaka, sai kuma kasar Mexico inda aka hallaka ‘Yan Jarida 11 a wannan shekara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.