Makaman Amurka ka iya kawar da bil'adama- Iran
Kasar Iran ta bayyana cewar sabon shirin gwamnatin Amurka na gina sabbin makaman nukiliya zai dada tabbatar da shirin kawar da bil'adama daga doran kasa.
Wallafawa ranar:
Wannan matsayi na gwamnatin Iran na zuwa ne bayan da shugaba Donald Trump ya bayyana cewar kasar za ta farfado da makamanta na nukiliya a matsayin mayar da martani kan barazanar da ke kunno kai daga Rasha.
Ministan Harkokin Wajen Iran Mohammed Javad Zarif ya ce, matakin ya saba wa yarjejeniyar kasashen duniya na hana yaduwar makami mai matukar hadari.
Zarif ya ce sabon matsayin na Amurka na nuna dogaro kan makamin nukiliyar wanda hakan babbar barazana ce ga rayuwar jama’a, yayin da ya zargi Amurka da zama bakin-ganga wajen zagon kasa ga yarjejeniyar da kasarsa ta kulla da kasashen yammacin duniya a karkashin Majalisar Dinkin Duniya.
Shi ma shugaba Hassan Rouhani ya bayyana matakin na Amurka a matsayin munafurci.
Kasashen Rasha da China da hukumar da ke hana yaduwar makamin duk sun bayyana damuwarsu akai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu