Isa ga babban shafi

Kasashe 8 sun bukaci samawa kabilar Rohingya makoma

Faransa, Birtaniya, Amurka da kuma wasu kasashe 5, sun bukaci kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ya tattauna kan makomar dubban ‘yan gudun hijirar Rohingya da aka kora daga kasar Myanmar.

Wasu 'yan gudun hijira, Musulmi 'yan kabilar Rohingya, yayin da suke jiran karbar abinci a sansaninsu da ke yankin Cox Bazaar a gaf da kasar Bangladesh.
Wasu 'yan gudun hijira, Musulmi 'yan kabilar Rohingya, yayin da suke jiran karbar abinci a sansaninsu da ke yankin Cox Bazaar a gaf da kasar Bangladesh. 路透社。
Talla

Hakan ya sa Majalisar tasayar da Talata mai zuwa, a matsayin ranar tattaunawa kan matsalar, bayan sauraron rahoto ko bayanin Kwamishinan da ke kula da ‘yan gudun hijira Fillipo Grandi.

Sama da ‘yan kabilar Rohingya 750,000 jami’an tsaron Myanmar suka raba da matsugunin su, sakamakon kisa da fyade da kuma kona gidajen su, abinda ya sa suka tsere zuwa kasar Bnagladesh domin samun mafaka.

Sauran kasashen da suka goyi bayan tattauna matsalar a kwamitin Sulhu, sun hada da Sweden, Poland, Nertherlands, Kazakhstan da kuma Equatorial Guinea.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.