Isa ga babban shafi
Myanmar

Amnesty international ta ja kunnen Myanmar kan 'yan Rohingya

Kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International ta ce sojojin Myanmar sun ci gaba da cin zarafin ‘yan kabilar Rohingya tare da azabtar da mata da kananan yara da kuma mazansu da yunwa, ta hanyar datse hanyoyin da za su kai ga samun abinci, domin tilasta musu tserewa daga kasar.

Yan kabilar Rohingya na jiran jami'an agaji na Red Cross
Yan kabilar Rohingya na jiran jami'an agaji na Red Cross 路透社。
Talla

Cikin rahoton da ta wallafa a baya bayan nan, Amnesty International ta ce har yanzu jami’an tsaron Myanmar sun ci gaba da kokarin shafe al’ummar Rohingya a arewacin jihar Rakhine.

Zuwa yanzu sama da mutane dubu 800 suka tsere zuwa kasar Bangladesh, bayan kaddamar da farmaki kansu da sojojin kasar suka yi a watan Agustan shekarar bara.

Kungiyar Amnesty ta ce jami’an tsaron Myanmar suna yi wa iyalan Rohingya fashi a shingayen bincike yayin da suke kokarin ficewa daga kasar, a lokaci guda kuma sun shiga kauyukansu inda suke sace mata, lamarin da ya kara jefa tsoro cikin ‘yan kabilar ta Rohingya.

Dangane da batun yunwa kuwa, Amnesty ta ce har ila yau jami’an tsaron kasar ta Myanmar ne suka haddasa ta da gangan, ta hanyar hana, ‘yan kabilar ta Rohingya, zuwa filayen nomansu, kasuwanni da kuma samun kai wa ga jami’an bada agaji da ke kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.