Amurka ta musanta ikirarin Netanyahu kan mamaye yankin Falasdinu
Amurka ta musanta ikirarin da Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya yi na cewa ya tattauna da ita kan wata doka da da za ta bashi damar mallake Yankunan Falasdinawa da ke Gabar Yamma da Kogin Jordan.Matakin da tuni Kasashen duniya suka fara kallon shi a matsayin yunkurin karshe na rushe duk wani shirin kafa kasar Falasdinu.
Wallafawa ranar:
Cikin 'Yan sa'o'i da sanarwar ta Benjamin Netanyahu kan shirin mallake Yankunan Gabar Yamma da Kogin na Jordan yayin wata ganawarsa da Yan Majalisu daga Jam’iyyar sa ta Likud, Amurkan ta musanta batun inda ta ce ko kadan basu tattauna makamanciyar maganar da shi ba.
Netanyahu dai ya ce yana shirya daukar matakin ne tare da kasar Amurka, saboda tasirin da take da shi ga kasar Israila.
Wannan mataki dai na zuwa ne kwana guda bayan Firaministan ya hana wasu Yan Majalisu biyu gabatar da irin wannan kudiri a gaban majalisar domin samun amincewar ta.
Masu sa ido kan siyasar Israila sun bayyana cewar daukan irin wannan mataki zai gamu da mummunar suka daga kasashen duniya, ko da yake hakan ba wani sabon abu bane ga Israila.
Tuni Kungiyar Falasdinu ta bayyana shirin a matsayin satar filayen su tare da hadin bakin Amurka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu