Isa ga babban shafi
Syria

Dakarun Syria sun kashe mutane sama da 100 a Ghouta

Hare-haren bama-bamai da dakarun gwamnatin Syria suka kaddamar sun kashe sama da mutane 100 da suka hada da kananan yara 30 a yankin gabashin Ghouta da ke hannun ‘yan tawaye.

Sama da mutane 100 sun mutu cikin kwanaki biyu a yankin gabashin Ghouta da ke Syria
Sama da mutane 100 sun mutu cikin kwanaki biyu a yankin gabashin Ghouta da ke Syria REUTERS/Bassam Khabieh
Talla

Kungiyar da ke sanya ido kan Syria da tawagar agaji sun tabbatar da alkaluman mamatan da aka bayyana a matsayin mafi muni tun bayan da aka yi wa yankin kawanya a shekarar 2013.

Har ya zuwa safiyar wannan Talata, rundunar tsaren fararen hula a Syria ta ce, an ci gaba da kaddamar da hare-haren bama-baman, in da sama da mutane 40 suka mutu.

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci kawo karshen hare-haren, in da ta ce sun wuce gona da iri.

A mnakon jiya ne yankin na Ghouta mai dauke da mutane kusan dubu 400 ya samu agajin farko a cikin watanni uku.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.