Isa ga babban shafi
Isra'ila

Isra'ila ta yi watsi da binciken kisan Falasdinawa a Gaza

Kasar Isra'ila taki amince wa da bukatar gudanar da bincike mai zaman kansa kan yadda sojojinta suka kashe Falasdinawa 16 da kuma jikkata daruruwa da ke zanga zangar lumana a kusa da iyakar Gaza da Isra'ila.

Sojin Isra'ila sun yi amfani harsashin gaske kan dandazon Falasdinawa da ke zanga-zangar neman 'yancin yankinsu da Isra'ila ta mamaye
Sojin Isra'ila sun yi amfani harsashin gaske kan dandazon Falasdinawa da ke zanga-zangar neman 'yancin yankinsu da Isra'ila ta mamaye REUTERS/Ibraheem Abu Mustafa
Talla

Firaminista Benjamin Netanyahu ya yaba wa sojojinsa saboda rawar da suka taka, yayin da Ministan tsaro, Avigdor Liebermann ya ce babu wani bincike da za a gudanar.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres da Shugabar Diflomasiyar Kasashen Turai Federico Mogherini sun bukaci gudanar da bincike kan lamarin.

Shugaban Falasdinu Mahmud Abbas yayi Allah wadai da kisan, in da kuma ya bukaci samar da tsaro a yankinsu.

"A yau ina bukatar Majalisar Dinkin Duniya da ta gagagauta samar da tsaro a yankinmu na Falasdinu mai ‘yanci, lura da irin kiyayya da ake nuna mana. Ina dora wa hukumomin Isra'ila cikakken laifin kisan mutanen da suka yi shahada a yau ta hanyar wutar da dakarunsu na mamaya suka bude mu su a yayin fuskantarsu da zanga-zangar lumana game da yankinsu." In ji Abbas.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.