Dubban mutane na tsare a hannun 'yan tawayen Libya
Wani sabon rahoto na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa, akwai wasu dubban mutane maza da mata da ba a taba jin labarinsu ba da ke ci gaba da kasancewa cikin mawuyacin hali a hannun kungiyoyin ‘yan tawaye masu dauke da makamai a Libya
Wallafawa ranar:
Rahoton wanda Hukumar Kare Hakkin Jama’a na Majalisar Dinkin Duniya ta fitar a wannan Talata, ya bayyana cewa, ‘yan tawayen na azabtar tare da cin zarafin wadannan bayin Allah da ke tsare a hannunsu.
Shugaban Hukumar Kare Hakkin Jama’ar, Zeid Ra’ad Al Hussein ya ce, dole ne a kawo karshen keta hakkokin jama’a da cin zarafinsu a Libya, sannan kuma a hukunta wadanda aka samu da laifi.
Tun dai a shekarar 2011 ne Libya ta tsindima cikin tashin hankali bayan kifar da gwamnatin marigayi Moammar Gaddafi, lamarin da ya bai wa kungiyoyin ‘yan tawaye damar cin karensu babu babbaka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu