Shugaban koriya ta arewa Kim Jong Un ya sanar da dakatar da gwajin makami nukiliya
Kim Jong Un Shugaban koriya ta arewa a kokarin sa na shirya tattaunawa da hukumomin Koriya ta Kudu a yau asabar ya sanar da dakatar da duk wani gwajin makaman nukiliya,tareda rufe wasu sassan da ake sarrafa ko gudanar da gwajin wadanan makamai..
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Shugaban Koriya ta arewa ya bayyana cewa kasar sa na da kyakkyawar manufa na gani an shiga tattauanawa da sauren kasashen Duniya irin su Koriya ta Kudu da Amurka.
Yan lokuta da sanar da haka, Shugaban Amurka Donald Trump ya yaba da wannan mataki tareda bayyana cewa yi haka daga Koriya ta arewa,ci gaba ne ga kasar ,da Duniya baki daya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu