Kasashe 5 sun yi watsi da sabon tsari kan yarjejeniyar yanayi ta Paris
Majalisar Dinkin Duniya ta amince da wani tsari da ke gabanta wanda a karon farko zai kai ga samar da karbabbiyar manufa kan muhalli, bisa yarjejeniyar da kasashen duniya suka kulla a taron rage dumamar yanayi ta Paris ta shekarar 2015.
Wallafawa ranar:
Mafi yawa daga cikin mambobi Kasashe 143 na Majalisar Dinkin Duniya, daga cikin kasashe 193 sun amince da wannan sabon tsari da kasar Faransa ta gabatar.
A bangare guda kuma kasashe 5 ne suka soki tsarin, wadanda suka hada da Rasha, Syria, Turkiya, Philippines da Amurka.
Haka zalika akwai kuma kasashen 7 da suka zama 'yan ba ruwanmu ciki har da kasar Iran sai kuma China da ta goyi bayan matakin.
A watan Satumba ne dai Shugaba Macron na Faransa, ya gabatar da bukatar daukan matakin, wadda zai kasance karon farko ke nan karkashin yarjejeniyar rage dumamar yanayi da kasashen duniya suka kulla a Paris.
Jakadiyar Amurka da ke Majalisar Dinkin Duniya Nikki Haley ta soki matakin, inda ta ke cewa Amurka ba za ta bada hadin kai ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu