Saudiya
Taron kungiyar kasashen Larabawa kan kisan Falesdinawa
Kasar Saudi Arabia ta kira taron kungiyar kasashen Larabawa gobe alhamis domin tattauna kisan gillar da Israila ta yiwa Falasdinawa sama da 60 ranar litinin.
Wallafawa ranar:
Talla
Kamfanin dillancin labaran MENA yace taron zai baiwa ministocin harkokin wajen kasashen tattauna matakin na Israila da kuma jaddada matsayin su na kin amincewa da matakin Amurka na bude ofishin Jakadancin ta a Birnin Kudus.
Ita ma Turkiya ta kira irin wannan taron, bayan ta kori Jakadan Israila da dake kasar ta, matakin da Israilan ta mayar da martani akai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu