Isa ga babban shafi
Koriya ta Arewa-Korea ta Kudu

An gana tsakanin Shugabanin Koriya ta Arewa da ta Kudu

Kasar Koriya ta Kudu tace shugaba Moon Jae In ya gana da takwaran sa na Arewa Kim Jong Un a iyakar da ta raba kasashen biyu, kwana guda bayan shugaban Amurka Donald Trump yace ana iya cigaba da shirin ganawar su a watan gobe.

Shugaba  Moon Jae-in na Koriya ta Kudu da Shugaba Kim Jong Un na Koriya ta Kudu
Shugaba Moon Jae-in na Koriya ta Kudu da Shugaba Kim Jong Un na Koriya ta Kudu Korea Summit Press Pool/Pool via Reuters
Talla

Fadar shugaba Moon Jae In tace shugabannin biyu sun kwashe sa’oi biyu suna ganawa a tsakanin su a kauyen Panmunjom, inda suka gana a watan jiya suka kuma bayyana aniyar su na kulla dangantaka mai karfi a tsakanin su.

Sanarwar tace shugabannin biyu sun tattauna hanyoyin aiwatar da yarjejeniyoyin da suka amince a Panmunjom da kuma tabbatar da nasarar ganawar da za’ayi tsakanin shugaba Donald Trump da Kim Jong Un a Singapore ranar 12 ga watan gobe.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.