Erdogan na ya karbi rantsuwar wa'adi na biyu
Shugaban Turkiya Recep Tayyip Erdogan ya yi rantsuwar ci gaba da jagorantar kasar wa’adi na biyu, a karkashin wani sauyi na kundin tsarin mulkin da ya ba shi karin karfin fada-a-ji da kuma aiwatar da sauye-sauye kai tsaye.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Bikin na yau na zuwa ne a dai dai lokacin da shugaban ya kori ma’aikata dubu 180 saboda zargin su da hannu a wani yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba.
Erdogan zai sha rantsuwar ne a zauren Majalisar Dokokin Kasar kafin daga bisani a rakashe a fadarsa tare da wasu tsirarun shugabannin kasashen duniya da suka halarci bikin.
‘Yan adawa na sukar salon mulkin Erdogan da suke kallo a matsayin kama-karya musamman ma a baya-bayan da aka samar da dokar da ta kara ma sa karfin ikon da wani shugaba a Turkiya bai samu a tsawon shekarun da suka shude.
Kusan shekaru biyu kenan da gwamnatin Erdoga ta yi nasarar dakile wani yunkurin juyin mulki a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu