Syria
Mutum 39 sun mutu a wata fashewa da ta faru a Syria
Wata fashewa a dakin ajiyar makaman ‘yan tawaye na Syria yau Lahadi ta hallaka akalla mutane 39 ciki har da yara kankana.
Wallafawa ranar:
Talla
Lamarin wanda ya faru a yankin arewa maso yammacin kasar a wani kauye da ke karkashin ikon ‘yan tawaye ya haddasa rugujewar akalla manyan gine-gine biyu.
Tuni dai jami’an agaji suka isa gurin don ceto mutanen da suka makale a baraguzan gine-gine sanadiyyar fashewar wadda kawo yanzu ba a gano abin da ya haddasa ta ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu