'Yan takarar shugaban kasa 13 zasu fafata a zaben Brazil
A kasar Brazil Lahadi suke gudanar da babban zaben kasar don zaben shugaban kasa, da kuma zabukan wakilan majalisar kasar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Duk wanda ya lashe zaben na gobe zai hau kujeran shugabancin kasa mai tattare da matsalolin cin hanci da rashawa da matsalolin tsaro.
Cikin ‘yan takara shugabancin kasar 13 kan gaba da ake ta zancensa shine Jair Bolsonaro wani tsohon kyaftin na soja, wanda yayi suna wajen sukan 'yancin mata, da masu luwadi da bakaken fata wanda kuma ya yi alkawarin tunkarar matsalolin cin hanci da rashawa da ayyukan hashsha da suka yiwa kasar katutu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu