Isa ga babban shafi
Amurka-Saudiya

Amurka ta soke takardun shiga kasar na wasu jami`an Saudiya

Amurka ta sanar da janye takardun shiga kasar da wasu mutane da ake zargin suna cikin wadanda suka kashe fitaccen dan jaridan Saudiya Jamal Kashoggi, a birnin Santambul na Turkiya.

Donald Trump Shugaban Amurka na magana dangane da kisan dan jaridan Saudiya
Donald Trump Shugaban Amurka na magana dangane da kisan dan jaridan Saudiya Reuters/路透社
Talla

Tun bayan da Saudiya ta amsa laifin kisan dan jaridan ne kasashen Duniya suka soma nuna damuwa tareda bukatar samun Karin haske dangane da kisan dan jaridan.

Mike Pompeo sakataren waje na Amurka ya bayyana cewa Amurka ta gamo mutane kusan dozen biyu dake da hannun wajen kisan dan jaridan.

Yace Amurka za ta kara daukan matakan hukunta mutanen da aka gano.

Yarima Ben Salmane ya dau alkawalin bayar da goyan baya zuwa ga masu bincike don gano gaskiyar abinda ya faru dangane da kisan dan jaridan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.