Isa ga babban shafi
Amurka-Saudiya

Sanata Graham ya bukaci a hukunta yarima Salmane

Daya daga cikin manyan yan Majalisar dattawan Amurka, sanata Lindsey Graham ya bayana cewar Yarima Muhammad bin Salman na Saudi Arabia na da hannu wajen kashe dan Jarida Jamal Khashoggi, saboda haka ya zama wajibi a hukunta shi.

Yarima Muhammad Ben Salmane na Saudi Arabia
Yarima Muhammad Ben Salmane na Saudi Arabia 路透社
Talla

Sanata Graham yace babu yadda za’ayi dangantaka tsakanin Amurka da Saudiya ta dore ba tare da hukunta Yarima Muhammad ba.

Dan Majalisa ya kuma bayyana shirin hukunta duk wadanda ake zargin suna da hannu wajen aikata kisan.

Tuni kasashen Amurka da Faransa da Canada suka sanya takunkumi kan mutane akalla 20 da ake zargin suna da hannu wajen aikata kisan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.