Netherlands
'Yan sandan Holland na laluben maharin Utrecht da ya hallaka mutum 1
Hukumomin Kasar Nertherlands sun ce su na farautar wani mutum da aka Haifa a Turkiya kan harin da aka kai Utrecht yau wanda yayi sanadiyar hallaka mutum guda.
Wallafawa ranar:
Talla
'Yan Sandan sun sanar da jama’ar birnin cewar, sun sanya ido kan mutumin Gokman Tanis mai shekaru 37 dangane da harin da aka kai yau da safe.
Rahotanni sun ce dan bindigar ya bude wuta kan jama’a inda ya kashe mutum guda, ya kuma jikkata wasu da dama.
Firaminista Mark Rutte ya bayyana harin wanda ke zuwa kwanaki kafin zaben kasar a matsayin abin tayar da hankali.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu