An gabatar da rahoton kutsen Rasha a zaben Amurka
Lauyan nan na musamman, Robert Mueller ya gabatar da rahotonsa kan zargin katsalandan din Rasha a lokutan yakin neman zaben Amurka na 2016 da zummar taimaka wa shugaba Donald Trump samun nasara.
Wallafawa ranar:
Yanzu haka, Ministan Shari’a na kasar, William Barr zai gabatar da rahoton ga Majalisar Dokokin Amurka bayan kammala nazari akai.
A cikin wata wasika da ya aika wa shugabannin Majalisar Dokokin, Mr. Barr ya shaida musu cewa, yana sa ran gabatar da musu da muhimman abubuwan da rahoton ya kunsa a wannan makon mai karewa.
Ana sa ran rahoton zai fayyace matakin da ya dace a dauka kan wadanda ke da hannu a katsaladan din.
Shugaba Trump da sauran mambobin jam’iyyar Republican sun sha bayyana binciken rahoton a matsayin bita da kullin siyasa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu