Koriya ta Arewa ta yi wa Amurka gargadi kan jirgin ruwanta
Kasar Koriya ta Arewa ta gargadi Amurka game da abinda ka iya faruwa biyo bayan kama mata jirgin ruwanta na dakon-kaya.
Wallafawa ranar:
Jakadan Koriya a Majalisar Dinkin Duniya, Kim Song ya shaida wa manema labarai cewar, kasarsa na sa ido kan matakan da Amurka ke dauka sakamakon kama jirgin mai suna Wise Honest.
Jakadan ya bukaci Amurka ta gaggauta sakin jirgin ruwan ko kuma ta zauna ta yi nazarin abinda zai biyo baya kan lamarin.
A ranar 9 ga watan nan Amurka ta sanar da kama jirgin ruwan saboda zargin da take yi cewar ana amfani da shi wajen safarar gawayi, lamarin da ya saba wa dokokin Majalisar Dinkin Duniya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu