Isa ga babban shafi
MDD

Mutane miliyan 70 sun tsere daga gidajensu saboda rikici

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa, sama da ‘yan gudun hijira miliyan 70 ne suka tsere daga gidajensu a bara sakamakon tashe-tashen hankula a kasashensu.

Wasu daga cikin mutanen da suka rasa muhallansu saboda rikice-rikice
Wasu daga cikin mutanen da suka rasa muhallansu saboda rikice-rikice REUTERS/Mohammad Ponir Hossain
Talla

A rahotonta na shekara-shakara, Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce, an ma takaita adadin mutanen da suka tsere daga gidajen nasu a shekarar 2018 saboda alkaluman da ta bayar basu kunshi daukacin ‘yan gudun hijirar Venezuela ba.

A karshen shekarar 2017 dai, mutane miliyan 68.5 ne aka kidaya cewa, an tilasta musu kaurace wa muhallansu saboda tashe-tashen hankula.

Sai dai a 2018, an samu karuwar ‘yan gudun hijirar saboda rikicin kabilancin da ya addabi kasar Habasha, da kuma matsalar tattalin arziki da ta dabaibaye Venezuela, abinda ya haifar da karancin abinci da magunguna a kasar.

Majalisar Dinkin Duniya ta kiyasta cewa, tun daga shekarar 2016, kimanin mutane miliyan 3.3 ne suka tsere daga Venezuela.

A halin yanzu dai, adadin ‘yan gudun hijira a duniya ya ninka a cikin shekaru 20 kuma ya zarce daukacin adadin mutanen kasar Thailand, yayinda kasashen Syria da Colombia ke kan gaba wajen fama da matsalar ta ‘yan gudun hijira.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.