A zuba wa Afrika jari don bunkasa kanta- Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci kasashen da suka ci gaba da su zuba jari a Afrika domin ganin ta samu ci gaba wajen tsayawa da kafafuwanta, wanda hakan zai magance rikice-rikice da kuma kaura zuwa kasashen duniya.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
A yayin da yake gabatar da jawabinsa a babban zauren Majalisar Dinkin Duniya, shugaban ya tabo batutuwa da dama da suka hada da matsalar tsaro da yadda masu tsatsauran ra’ayi ke amfani da kafofin sada zumunta suna aikata laifuka da yaki da cin hanci da rashawa da muhimmancin bada ilimi da kuma tallafa wa marasa karfi.
Shugaban ya bayyana samar da kasar Falasdinu mai cin gashin kanta a matsayin muhimmiyar hanyar warware rikicinta da Isra'ila.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu