Isa ga babban shafi
Faransa

Macron na ganawa da shugabannin Sahel kan ta'addanci

Yau Litinin shugabannin kasashen yankin Sahel ke ganawa da takwaransu Emmanuel Macron a garin Pau da ke kudu maso yammacin Faransa don tattauna yadda za a tunkari matsalar ayyukan ta’addanci a yankin Sahel.

Emmanuel Macron tare da shugabannin kasashen yankin Sahel
Emmanuel Macron tare da shugabannin kasashen yankin Sahel REUTERS/Ludovic Marin
Talla

Hudu daga cikin shugabannin kasashen na yankin Sahel biyar ne aka tabbatar da cewa za su halarci wannan taro da za a fara a marecen yau, sai kuma wasu manyan baki kamar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, da shugaban Hukumar Tarayyar Afrika Moussa Faki, sai shugaban Majalisar Turai Charles Michel.

Macron ya gayyaci shugabannin kasashen biyar don halartar wannan taro ne a daidai lokacin da ake samun kiraye-kirayen ganin cewa Faransa ta janye dakarunta da yawunsu ya kai dubu 4 da 500 daga yankin na Sahel.

To sai dai duk da kasancewar wadannan sojoji, kusan a kowace safiya ana samun yawaitar hare-hare tare da samun asarar rayukan mutane masu tarin yawa.

Harin baya-bayan nan, shi ne wanda aka kai wa barikin sojin Chinagoder da ke Jamhuriyar Nijar, inda sojoji 89 suka rasa rayukansu.

Ko a ranar Juma’a dubban mutane sun gudanar da tarzomar neman ganin sojojin Faransa sun fice daga kasar Mali.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.