Guinea
Kungiyar Turai Ta Gamsu Da Zabe
Masu sa idanu daga Kungiyar Tarayyar Turai akan babban zaben da akayi akasar Guinea sunce sun gamsu da yadda aka gudanar da zaben.Har ya zuwa yammacin Laraba Hukumar Zaben kasar bata fito fili da sakamakon babban zaben kasar ba.‘Yan adawa da sauran kungiyoyi da dama sun soki zaben da cewa an tafka magudi.Jagoran masu sa idanu akan zaben da akayi ranar Lahadi data gabata, Alexander von Lambsdorff ya fadawa manema labarai cewa duk da wasu matsaloli da aka fuskanta zaben ya gamsar dasu.
Wallafawa ranar: