Isa ga babban shafi
Cote d’ivoire

Zamu ci gaba da haramta fita da Cocoa, inji Ouattara

Shugaban kasar Cote d’Ivoire mai jiran gado Alassane Ouattara ya bayyana cewa zasu kara wa’adin haramcin fita da Cocoa daga kasar a matakin da suka dauka tun da farko na tsawon wata guda idan har abokin hamayyarsa Laurent Gbagbo ya ki amincewa ya sauka daga madafan ikon kasar.A wata hira da shugaban ya yi da kafafen yada larabarai, mista Ouattara yace a shirye ya ke ya yi amfani da takunkumi a fannin tattalin arziki domin tursasawa Laurent Gbagbo ban kwana da madafan iko.Alassane Ouattara shi ne dai hukumar zaben kasar ta bayyana a matsayin wanda ya lashe zaben kasar da aka gudanar a watan Nuwambar bara, kuma wanda kasashen duniya suka amince da shi a matsayin shugaban kasar Cote d’Ivoire inda kuma Laurent Gbagbo ya ki amincewa ya sauka bayan ya sha kaye a zaben.A 23 ga watan Janairun bana ne Mista Ouattara ya haramta fita da Cocoa a kasar na tsawon wata daya inda a yanzu yake tunanin ci gaba da wannan matakin domin kawo karshen takaddamar ja-in-jar shugabanci tsakaninsa da Laurent Gbagbo.  

Alassane Ouattara lokacin da yake zantawa da kafar yada labaran kasar Faransa ta France 24.
Alassane Ouattara lokacin da yake zantawa da kafar yada labaran kasar Faransa ta France 24. France 24
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.