Cote d’Ivoire
Tsohuwar jam'iyya mai mulkin Cote d'Ivoire ta nemi kawo karshen tashin hankali
Jam’iyyar tsohon shugaban kasar Cote d’Ivoire Laurent Gbagbo ta Ivorian Popular Front, ta nemi kawo karshen tashe tashen hankulan kasar daga kungiyoyi masu dauke da makamai.Shugaban jam’iyyar Pascal Affi N’Guessan tilas yaki ya kawo karshe, domin sake gina kasa.A ranar Litinin data gabata dakarun dake biyayya wa shugaban kasar ta Cote d’Ivoire Alassane Ouattara suka cafke Mr Gbagbo, wanda ya ci gaba da riek madafun iko, bayan faduwa a zabe.
Wallafawa ranar: