Isa ga babban shafi
Chadi

Yan kasar Cadi masu gudun hijira kan zaben kasar

Zaben shugaban kasar Cadi da aka gudanar jiya Litinin, ya nuna shugaba Idriss Deby zai samu nasara karo na hudu, bayan ‘yan adawa sun kauracema zaben.Mafiyawancin mazabu sun kasance wayam, amma kawo yanzu babu adadin wadanda suka fita jifa kuri’un na su ,daga cikin masu zabe mutane milyan biyar.Idrissa Deby Itno ya na mulkin kasar ta Cadi tun bayan juyin mulkin shekarar ta 1990.Tuni tsaffin kungiyoyin ‘yan tawaye da ke gudun hijira a wajen kasar suka yi watsi da sakamakon zaben, kamar yadda Kanal Jibrin Ibrahim tsohon dan tawaye ke cewa. 

Shugaba Idriss Deby Itno na Cadi wajen jefa kuri'ar shi ta zaben shugaban kasa
Shugaba Idriss Deby Itno na Cadi wajen jefa kuri'ar shi ta zaben shugaban kasa AFP PHOTO/Gael COGNE
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.