Najeriya
Jama’iyar CPC mai adawa a Najeriya ta shigar da kara a kotu kan zaben da ya gudana
Yau Litinin jam’iyyar adawa ta CPC dake tarayyar Najeriya ke shigar da kara a kotu, domin kalubalantar zaben shugaban kasa da ya gudana a watan jiya. Dan takarar jam’iyyar Janar Mahammadu Buhari ya zo na biyu, yayin da Goodluck Jonathan ya lashe zaben, kamar yadda hukumar zabe ta aiyana.Mataimakin shugaban jam’iyyar ta CPC na kasa, Mustapha Salihu ya shaida mana da dalilansu.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: