Libya
Akwai fargabar yaduwar makaman kasar Libya a Yankin Sahel
YAU ne aka shiga rana ta biyu, a taron da ake kan tsaro da samar da zaman lafiya a kasar Algeria, wanda ke samun halartar kasashen Niger, Mali, Algeria da Mauritaniya, da kuma wakilan kasashen kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya.Kwamandan sojin Amurka a Afrika, Janar Carter Han, ya bayyana fargabar su kan yaduwar makaman Libya, a Yankin Sahel, inda ya ce, “muna fatar samo hanyar magance cigaba da yaduwar makamai, da bama bamai a Yankin Sahel, da kuma damuwarmu kan kungiyoyin Yan ta’adda a Gabashi da Tsakiyan Afrika, da kuma na Yankin na Sahel.”
Wallafawa ranar: