Isa ga babban shafi
Najeriya

‘Yan Majalisa sun juya wa Jonathan baya a Najeriya

Yunkurin shugaban Najeriya Gooodluck Jonathan na kokarin sasantawa da Majalisar kasar domin neman amincewarsu ga shirinsa na janye tallafin man Fatir ya gamu da cikas bayan da aka tashi baram-baram a zaman taron shugaban da ‘Yan majalisun.

Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan
Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan REUTERS/ Daniel Munoz
Talla

03:58

Hon Ado Alhassan Doguwa

Jonathan ya kira taron gaggawa ne domin ganawa da Sanatoci 109 da ‘yan majalisar wakilai 360 a fadarsa domin tattauna muhimmacin janye tallafin man Fetir, tare da tattauna hanyoyin magance matsalar tsaro musamman rikicin kungiyar Boko Haram.

An samu sabani ne dai bayan da shugaban ya bayyana cewa shirin janye tallafin Man Fetir shi ne mafita ga Najeriya. Daga nan ne kuma ‘yan majalisun suka fara shewar kin amincewarsu.

00:32

Sen Ali Ndume

A lokacin da yake jawabi kakakin majalisar wakilai Aminu Waziri Tambuwal yace Majalisar zata taimaka wajen shawo kan matsalar tsaro a cikin kasar amma sauran bukatun shugaban sai majalisa ta koma zauren muhawararta kafin su dauki matsayi akai.

Gayyatar ta shugaban na zuwa ne bayan da wasu mambobin majalisar suka fara barazar kada kuri’ar tsige shugaban saboda halin matsalar tsaro a Najeriya.

00:41

Hon. Yusuf Bala

Yanzu haka kuma ‘Yan majalisun sun juyawa shugaban baya sai dai ministan yada labaran kasar Labaran maku yace gwamnatin zata ci gaba da tattaunawa da ‘yan majalisun domin neman amincewarsu.

00:28

Kalaman Labaran Maku, Ministan yada labaran Nigeria

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.