Isa ga babban shafi
Cote d’Ivoire

Magoya bayan Tsohon Shugaban Cote d'Ivoire Gbagbo sun ji dadin rashin fitowar masu zabe

An smau karancin fitowar masu zabe, yayin zaben ‘yan majalisun kasar Cote d’Ivoire da aka gudanar ranar Lahadi da ta gabata.

Mai zabe na kasar Cote d'Ivoire
Mai zabe na kasar Cote d'Ivoire
Talla

Mai magana da yawun jam’iyyar tsohon Shugaban kasar Laurent Gbagbo, mai suna Justin Kone Katinan ya ce wannan zai tabbatar da rashin ingancin gwamnatin Shugaba Alassane Ouattara.

Hukumar zaben kasar ta Cote d’Ivoire ta bayyana cewa an samu fitowar masu zabe na kusan kashi 35 cikin 100.

Jam’iyyar tsohon Shugaba Gbagbo tana kauracewa zaben domin nuna rashin jin dadin yadda aka mika Gbagbo wa kotun duniya dake hukunta masu laifukan yaki dake birnin Hague.

Dakarun kiyaye zaman lafiya na MDD
Dakarun kiyaye zaman lafiya na MDD Reuters / Thierry Gouegnon

Cikin tsakiyar wannan makon ake saran samun cikekken sakamakon zaben. Dakarun kiyaye zaman lafiya na kasashen duniya suna gudanar da sintiri domin tabbatar da zaman lafiya tare da 'yan sandan kasar. Kuma babu wani rohoto na tashin hankali kawo yanzu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.