Isa ga babban shafi
Habasha

A Ranar Biyu ga watan Satumba za’a binne Zenawi

Gwamnatin kasar Habasha tace a ranar Biyu ga watan Satumba za’a binne tsohon Firaministan kasar Meles Zenawi wanda ya mutu a ranar Litinin a birnin Brussels bayan kwashe lokaci yana rashin lafiya.Daruruwan Habashawa ne suka yi zaman makokin mutuwar Shugaban bayan kawo gawarsa zuwa Addis Ababa daga Brussels a ranar Talata. Yanzu haka gawarsa an ajiye ta a cikin gidansa kafin bukin binne shi.

Al'ummar kasar Habasha suna zaman makokin mutuwar shugabansu  Meles Zenawi.
Al'ummar kasar Habasha suna zaman makokin mutuwar shugabansu Meles Zenawi. REUTERS/Siegfried Modola
Talla

Mataimakin Firaminista Hailemariam Desalegn zai jagoranci gwamnatin rikon kwarya har 2015 bayan an gudanar da zabe. Ana sa ran rantsar da shi nan bada dadewa ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.