Isa ga babban shafi
Faransa

An kara kashe wani sojan Faransa daya a Mali

Ma’aikatar tsaron kasar Faransa ta tabbatar da mutuwar wani sojanta daya a Mali inda yanzu haka Faransar ke jagorantar fada da ‘yan tawaye a Arewacin kasar.

Wani sojan Faransa a arewacin kasar Mali
Wani sojan Faransa a arewacin kasar Mali
Talla

Ministan tsaron Faransa Jean-Yves le Drian, ya ce sojan kasar dan kimanin shekaru 24 a duniya mai suna Alexandre Van Dooren, ya hadu da ajalinsa ne a lokacin yake gudanar da aikin share abubuwa masu fashewa da ‘yan tawaye suka binne a kusa da yankin Tessalit da ke gab da iyakar kasar Mali da kuma Aljeriya.

Har ila yau wasu majiyoyi na kusa da ma’aikatar tsaron ta Faransa, sun ce ko baya ga sojan daya da ya hadu da ajalinsa, akwai kuma wasu sojojin biyu da ke cikin mummunan yanayi sakamakon raunukan da suka sama.

A jimilce dai sojojin Faransa biyar ne suka rasa rayukansu daga lokacin da suka shiga kasar ta Mali domin fada da abin da Faransar ta kira shi da suna ta’addanci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.