Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

Kasashen Tsakiyar Afirka sun yi watsi da Djotadia a matsayin shugaba

Shugaban kasar Chadi, Idris Deby, ya ce taron shugabannin kasashen da ke Tsakiyar Afirka, ya ki amincewa da shugaban ‘Yan Tawayen Seleka Michel Djotodia, wanda ya kwaci mulki da karfi a matsayin Shugaban Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya.

Shugaban Chadi, Idriss Déby
Shugaban Chadi, Idriss Déby Photo AFP / Bertrand Guay
Talla

Bayan taron da shugabannin suka yi a birnin Ndjamena, shugaba Deby ya ce ba za su amince da Michel Djotodia ba, a matsayin jagora kasar.

Shugaban na Chadi ya ci da cewa, za’a kafa wani kwamitin fitattun mutanen kasar ne da zai jagoranci gwamnatin rikon kwarya, kana kwamitin ne zai zabo shugaba, wanda zai shirya zabe a cikin watanni 18 da za su biyo baya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.